fidelitybank

Abba ka nemi afuwar Daurawa – Dr. Abdallah Usman Gadon Kaya

Date:

Saukar fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa daga muƙaminsa na shugaban hukumar Hisbah na ci gaba da janyo ce-ce-ku-ce, inda fitaccen malamin addinin Musulunci, Dr. Abdallah Usman Gadon Kaya ya shawarci gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya nemi afuwar Malam Aminu Daurawa.

Gadon Kaya ya yi wannan kira ne a wani bidiyo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta na facebook.

Ya ce “Muna kira ga gwamna Abba Yusuf da waɗanɗa ke kusa da shi su kai zuciya nesa su kira malam Daurawa, su zauna da shi kuma su ba shi haƙuri kan abubuwan da ya faru.”

A safiyar Juma’a ne Sheikh Aminu Daurawa ya sanar da saukar sa daga muƙamin shugaban Hisbah ta jihar Kano.

Daurawa ya ce ya yi hakan ne bayan wasu kalamai da gwamnan jihar Abba Kabir ya furta a ranar Alhamis, waɗanda suka karya masa gwiwa.

A bidiyon nasa, Sheikh Abdallah Gadon Ƙaya ya ce ya kamata gwamna Abba Yusuf ya duba al’ummar jihar Kano da ci gaban da malam Daurawa ya kawo da kuma gudummawar ya yake bai wa ita gwamnatin ta Kano.

“Ya kamata a zauna da shi malam Daurawa a ba shi shawarwari a kan abubuwan ya yake yi ko ake ta cewa Hisbah take yi.” in ji Gadon Kaya.

“Matsayin malam Daurawa ya kai kuma darajarsa ta kai.”

Gadon Kaya ya ce yana bayar da shawarar ce saboda ci gaban jihar Kano da ci gaban gwantin gaba ɗaya.

Hisbah dai ta riƙa shan suka daga wasu ɓangarori na al’umma bayan da wani faifan bidiyo ya yaɗu a shafukan sada zumunta, inda aka ga jami’an hukumar na jefa wasu matasa da ake zargi da aikata ‘rashin tarbiyya’ cikin mota.

Sai dai ana kallon ajiye aikin Sheikh Daurawa, wanda ɗaya ne daga cikin malamai mafiya shahara a arewacin Najeriya a matsayin koma-baya ga yunƙurin tabbatar da ɗa’a a jihar ta Kano, kuma wani mummunan tabo ga gwamnatin gwamnan jihar Abba Kabir Yusuf.

news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp