Biyo bayan zaben fidda gwani na gwamna na jam’iyyar New Nigerian Peoples Party (NNPP), Alhaji Abba Kabir Yusuf, mai biyayya ga Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya zama dan takarar gwamna a jam’iyyar a zaben 2023 mai zuwa.
Zaben fidda gwanin wanda ya gudana a dakin taro na Sani Abacha Youth Centre da ke Kano a jiya, kwamitin jam’iyyar karkashin jagorancin Sanata Musa Bako Aujara daga kungiyar ta kasa ne ya gudanar da zaben.
Ya shaida wa manema labarai cewa, Yusuf ne kadai ke takara a matsayin dan takarar gwamna a jam’iyyar NNPP a jihar Kano, kuma bisa ka’idojin zabe na jam’iyyar, wakilai za su tabbatar da shi ko a’a.
Musa ya bayyana cewa, wakilai 1,452 da uku daga kowace unguwanni 484 za su tabbatar da takararsa.