Jam’iyyar APC ta yi kira ga jama’a da su yi watsi da duk wani jadawalin zaben fidda gwani na jam’iyyar, saboda har yanzu ba a fitar da ko daya ba.
Jam’iyyar ta musanta hannu ko kuma ta san jadawalin zaben fidda gwanin da aka yi ta yadawa a shafukan sada zumunta da kuma wasu kafafen yada labarai.
Sakataren yada labarai na jam’iyyar APC na kasa, Felix Morka, ne ya bayyana hakan ga manema labarai a gidan Buhari, sakatariyar jam’iyyar ta kasa, inda ya ce, kwamitin ayyuka na kasa ya fara tattaunawa a kan lamarin a ranar Talata, amma har yanzu ba ta kai ga yanke hukunci ba.
Morka ya kuma lura cewa, jam’iyyar za ta sanar da masu ruwa da tsaki da daukacin ‘yan Najeriya idan aka kammala ainihin jadawalin.