fidelitybank

A yi taka-tsan-tsan a kan hukuncin zaben gwamnan Kano – Shehu Sani

Date:

Tsohon dan majalisar tarayya, Sanata Shehu Sani ya bukaci a yi taka-tsan-tsan wajen tunkarar shari’ar da ake yi kan zaben gwamnan jihar Kano.

Hakan na zuwa ne yayin da ya yi zargin cewa hukuncin kotun daukaka kara na CTC da ke yaduwa ya tabbatar da nasarar Gwamna mai ci.

A cewarsa, “Al’amarin Kano gurneti ne, kuma dole ne a kula da fintinkau da matuƙar kulawa.”

Sani ya bayyana ra’ayinsa ne a wani rubutu da ya wallafa a dandalinshi na sada zumunta na X, ranar Talata.

Tsohon dan majalisar ya bayyana cewa “dimokradiyya ba za ta ci gaba da wanzuwa ba yayin da muradun siyasa suka keta hakkin ɗabi’a da tsarin mulki na tabbatar da gaskiya da kuma ƙa’idodin adalci.”

Ya rubuta cewa, “Kano: Hukuncin Kotun Daukaka Kara ta CTC a fili ya tabbatar da nasarar Gwamna mai ci.

“Al’amarin Kano gurneti ne, kuma dole a kula da fintinkau da matuƙar kulawa. Dimokuradiyyarmu ba za ta ci gaba da wanzuwa ba yayin da muradun siyasa suka mamaye ayyukanmu na kyawawan halaye da tsarin mulki na tabbatar da gaskiya da ka’idojin adalci.”

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta amince da hukuncin da kotun sauraron kararrakin zabe ta jihar Kano ta yanke, wanda ya soke nasarar Abba Yusuf na jam’iyyar New Nigeria People’s Party, NNPP.

Kwamitin mai mutane uku karkashin jagorancin mai shari’a Moore Adumein, ya bayyana Nasiru Gawuna na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), a matsayin wanda ya cancanta ya lashe zaben gwamnan jihar da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp