fidelitybank

A yi taka-tsan-tsan a kan hukuncin zaben gwamnan Kano – Shehu Sani

Date:

Tsohon dan majalisar tarayya, Sanata Shehu Sani ya bukaci a yi taka-tsan-tsan wajen tunkarar shari’ar da ake yi kan zaben gwamnan jihar Kano.

Hakan na zuwa ne yayin da ya yi zargin cewa hukuncin kotun daukaka kara na CTC da ke yaduwa ya tabbatar da nasarar Gwamna mai ci.

A cewarsa, “Al’amarin Kano gurneti ne, kuma dole ne a kula da fintinkau da matuƙar kulawa.”

Sani ya bayyana ra’ayinsa ne a wani rubutu da ya wallafa a dandalinshi na sada zumunta na X, ranar Talata.

Tsohon dan majalisar ya bayyana cewa “dimokradiyya ba za ta ci gaba da wanzuwa ba yayin da muradun siyasa suka keta hakkin ɗabi’a da tsarin mulki na tabbatar da gaskiya da kuma ƙa’idodin adalci.”

Ya rubuta cewa, “Kano: Hukuncin Kotun Daukaka Kara ta CTC a fili ya tabbatar da nasarar Gwamna mai ci.

“Al’amarin Kano gurneti ne, kuma dole a kula da fintinkau da matuƙar kulawa. Dimokuradiyyarmu ba za ta ci gaba da wanzuwa ba yayin da muradun siyasa suka mamaye ayyukanmu na kyawawan halaye da tsarin mulki na tabbatar da gaskiya da ka’idojin adalci.”

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta amince da hukuncin da kotun sauraron kararrakin zabe ta jihar Kano ta yanke, wanda ya soke nasarar Abba Yusuf na jam’iyyar New Nigeria People’s Party, NNPP.

Kwamitin mai mutane uku karkashin jagorancin mai shari’a Moore Adumein, ya bayyana Nasiru Gawuna na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), a matsayin wanda ya cancanta ya lashe zaben gwamnan jihar da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp