Tsohon dan majalisar tarayya, Sanata Shehu Sani ya bukaci a yi taka-tsan-tsan wajen tunkarar shari’ar da ake yi kan zaben gwamnan jihar Kano.
Hakan na zuwa ne yayin da ya yi zargin cewa hukuncin kotun daukaka kara na CTC da ke yaduwa ya tabbatar da nasarar Gwamna mai ci.
A cewarsa, “Al’amarin Kano gurneti ne, kuma dole ne a kula da fintinkau da matuƙar kulawa.”
Sani ya bayyana ra’ayinsa ne a wani rubutu da ya wallafa a dandalinshi na sada zumunta na X, ranar Talata.
Tsohon dan majalisar ya bayyana cewa “dimokradiyya ba za ta ci gaba da wanzuwa ba yayin da muradun siyasa suka keta hakkin ɗabi’a da tsarin mulki na tabbatar da gaskiya da kuma ƙa’idodin adalci.”
Ya rubuta cewa, “Kano: Hukuncin Kotun Daukaka Kara ta CTC a fili ya tabbatar da nasarar Gwamna mai ci.
“Al’amarin Kano gurneti ne, kuma dole a kula da fintinkau da matuƙar kulawa. Dimokuradiyyarmu ba za ta ci gaba da wanzuwa ba yayin da muradun siyasa suka mamaye ayyukanmu na kyawawan halaye da tsarin mulki na tabbatar da gaskiya da ka’idojin adalci.”
Kotun daukaka kara da ke zamanta a Abuja ta amince da hukuncin da kotun sauraron kararrakin zabe ta jihar Kano ta yanke, wanda ya soke nasarar Abba Yusuf na jam’iyyar New Nigeria People’s Party, NNPP.
Kwamitin mai mutane uku karkashin jagorancin mai shari’a Moore Adumein, ya bayyana Nasiru Gawuna na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), a matsayin wanda ya cancanta ya lashe zaben gwamnan jihar da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.