Gwamnatin tarayya ta ce, tashar ruwan Lekki Deep Sea Port, da ke jihar Legas za ta fara gudanar da harkokin kasuwanci gaba daya a watan Satumba.
Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, yayin da yake duba aikin a ranar Asabar a Legas, ya ce, wannan babbar nasara ce ga gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari.
Amaechi ya ce: “A matsayina na ɗan boko, ba zan iya yin magana bisa kaso ba. Zan iya cewa abin ya burge ni idan aka kwatanta da na ƙarshe da muka zo nan.
“Hukumomin sun shaida min cewa ya zuwa watan Yuni, suna jiran manyan motoci, kuma a watan Satumba, kamar yadda muka amince, su fara harkokin kasuwanci, na ji dadi.
“Wannan aiki ne na sirri, da lokaci mai tsawo za su tattara kudaden shiga daga harkokin kasuwanci kafin su mikawa Gwamnatin Tarayya ta hannun NPA.
“Tabbas za a karbi haraji a nan, hatta su ma za su biya haraji. In ji Rotimi.