Tsohon babban dogarin shugaban mulkin soja, marigayi Janar Sani Abacha, wato Manjo Hamza Al-mustapha, ya ce, idan har ya zama shugaban kasa, a cikin wata shida zai kawo karshen matsalar tsaro ta Boko Haram da ta addabi Najeriya.
Almustapha ya ce, zai je ya tare a dajin Sambisa, da ke jihar Borno, inda nan ne ake ganin matattarar mayakan Boko Haram, tsawon sati daya, domin daukar duk matakin da ya wajaba a dauka domin ganin karshen mayakan.
Ya ce idan har ya zama shugaban kasa to lalle ne abin Allah ya shimfida za a yi wa dole ne a yi shi, ya ce, ”komai zafinsa a idon ko su waye”, yana mai bayar da misali da matsalar tsaron da kasar ke fama da ita.
Tsohon dogarin na Abacha yana magana ne a hira ta musamman da BBC, inda ya bayyana shigarsa jerin masu neman takarar shugabancin kasar a zaben da za a yi a shekara mai zuwa ta 2003, inda zai nemi takara a karkashin jam’iyyar Action Alliance.