Kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ) a ranar Juma’a ta shaida wa gwamnati, jam’iyyu da ‘yan siyasa da su tabbatar an kare ‘yan jarida a zaben 2023.
Shugaban NUJ, Chris Isiguzo ne ya yi wannan kiran a Gombe a wani taron karawa juna sani ga manema labarai a yankin Arewa maso Gabas. Isiguzo ya koka da yadda ‘yan jarida suka rasa rayukansu, suka samu raunuka ko kuma aka lalata musu kayan aikinsu yayin da suke gudanar da zabuka amma duk da haka ba a yi wani abu ba don tabbatar da daukar alhakin kai hare-hare kan kafafen yada labarai tsawon shekaru.
Isiguzo, wanda mataimakinsa Alhassan Yahya ya wakilta, ya bukaci masu ruwa da tsaki da su dakile kai hare-hare kafin da kuma lokacin zabe.
“Yana da muhimmanci gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki su baiwa batun tsaro da kulawar da ake bukata.
“Tsaron ‘yan jarida yana da mahimmanci wajen neman hakkin farar hula, siyasa, tattalin arziki, zamantakewa da al’adu na dukkan ‘yan kasa,” in ji shi.
Sai dai kungiyar ta NUJ ta bukaci ‘yan Najeriya da su taka rawar gani a zaben 2023.