Yayin da Isra’ila ke kai hare-hare a Lebanon da Gaza, har yanzu yankin na dakon ganin yadda – ko yaushe – za ta kai wa Iran hari.
A ranar 1 ga Oktoba, Iran ta harba maƙamai masu linzami kusan 200 zuwa Isra’ila, sai dai an kakkaɓo mafi yawansu.
A lokacin, Firaiministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya ce Iran “za ta ɗanɗana kudarta” – amma har yanzu babu wani martani na soji.
Ministan harkokin wajen Iran ya tattauna da babban sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya Antonio Guterres a daren jiya – ya kuma ce Iran a shirye take ta mayar da martani idan Isra’ila ta kai mata hari.
“Iran, yayin da take ƙoƙarin kare zaman lafiya da tsaro a yankin, ta shirya tsaf don mayar da martani mai tsauri kan duk wata kasada ta Isra’ila,” kamar yadda Abbas Araghchi ya faɗa wa Guterres, a cewar ma’aikatar harkokin wajen Iran.