fidelitybank

A shirye na ke na sadaukar da raina don kawo ƙarshen Ƴan Ta’addan Katsina – Raɗɗa

Date:

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya ce zai iya sadaukar da rayuwarsa domin kawo karshen matsalar ‘yan bindigar da suka addabi jiharsa.

Cikin wata hira da BBC, Gwamna Radda ya ce bangaren tsaro shi ne ya fi kowanne muhimmanci kuma tuni suka fahimci hakan shi ya sa ma aka yi doka don a kafa rundunar ‘yan sa-kai tare da ba su makamai da nufin taimaka wa jami’an tsaro.

Ya ce,” To yanzu mun kaddamar da su, mun horar da su mun ba su kayan aiki mun ba su motoci da babura da ma motoci masu sulke.”

Gwamnan na Katsina, ya ce dangane da batun biyansu kudaden alawus, gwamnatinsa ta dauki tsarin mafi karancin albashi wanda da shi ne za a rinka biyan ‘yan sa-kan alawus.

Dikko Radda, ya ce, “ Wani abu da ya kamata kuma mutane su sani, shi ne su wadannan ‘yan sa-kan su ne wadanda a garuruwansu suke irin wannan aiki ba tare da an biya su ko sisi ba, kuma suna wadannan ayyuka ne saboda su kare mutuncin iyayensu da ‘yan uwansu da kuma danginsu.”

Ya ce, “ Batun da wasu ke yi cewa irin wadannan ‘yan sintiri su ke kara dagula al’amura a harkar tsaro, zance ne na banza domin duk wanda ke zaune a wuraren da ke fama da matsalar tsaro ya san abin da ke faruwa, ta yaya za a kare mutanen da ke sace mutane su ci mutuncinsu da kashesu, ai ba abu ne mai wuya ba.”

Gwamnan na Katsina, ya ce,” Wallahi tallahi a matsayina na gwamna sai dai raina ya fita ba zan yarda wani ya zo ya ci mutane ba bayan ina da yadda zan yi, don wannan matsala ta kai halin da dole a hada kai domin ganin cewa an kawo karshen wannan matsalar don matsala ce da ta dame mu.”

Ya ce, “Duk wanda ke wani surutu akasin hakan saboda ba ‘yan uwansa ake kashe wa ba ne shi ya sa.”

Gwamna Radda ya ce, “ Kuma nan ba da jimawa ba idan an kammala duk shirye-shiryen da suka dace za a fara shiga daji da ni ma.”

tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp