fidelitybank

A shirye na ke na gana da ƴan sandan Najeriya kuma bani da biyar hamɓarar da Tinubu – Ɗan Birtaniya

Date:

Andrew Wynne, dan kasar Birtaniya, wanda rundunar ‘yan sandan Najeriya ta bayyana cewa yana neman hambarar da gwamnatin shugaba Bola Tinubu, ya ce ba guduwa ya yi ba.

Ƴan sanda sun bayyana Wynne da wani dan Najeriya, wani Lucky Ehims da ake nema ruwa a jallo, ya ba su kyautar Naira miliyan 20.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar, ACP Muyuwa Adejo, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya ce duk wanda ya samu labarin da ya kai ga cafke mutanen biyu, za a ba shi tukuicin Naira miliyan 10 ga kowane daya daga cikin wadanda ake zargin.

Sai dai da yake magana kan lamarin a wani shirin gidan talabijin na Channels a ranar Litinin, Wynne ya ce a shirye yake ya tattauna da ‘yan sandan Najeriya.

Da yake musanta zargin, dan kasar Birtaniya ya bayyana cewa, ba zai iya yin wata makarkashiya don tada zaune tsaye a shugabancin gwamnatin Najeriyar ba, yana mai cewa ya shafe sama da shekaru 25 yana ziyartar kasar.

Ya bayyana shirin sa na ganawa da jami’an hukumar ta Najeriya a birnin Landan domin tattaunawa kan wannan zargi.

Ya ce, “Ban san cewa ni mai gudu ba ne. Ban san cewa ina guje wa doka ba.

“Na kai ziyara Najeriya tsawon shekaru 25 kuma na yi kantin sayar da littattafai a ofishin NLC da ke tsakiyar Abuja tsawon shekaru bakwai. A duk tsawon lokacin, tabbas jami’an tsaro ba su biya ni ba.

“Na fi farin cikin yin magana da ‘yan sanda da tattaunawa ta WhatsApp ko Zoom.

“Na fi farin cikin zuwa Landan na gana da jami’ai a babban hukumar Najeriya a Ingila.”

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp