fidelitybank

A shirye muke mu haɗa kai da sojoji don magance shaye-shaye a Kano – NDLEA

Date:

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, ta ce a shirye ta ke ta hada kai da sojojin Najeriya wajen yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi a jihar Kano.

Hakan ya fito ne daga bakin jami’in hulda da jama’a na hukumar, Sadiq Muhammad-Maigatari ranar Alhamis a Kano.

Sanarwar ta ce kwamandan hukumar ta NDLEA a jihar, Mista Abubakar Idris-Ahmad, ya bayyana haka a lokacin da sabon kwamandan 3 Brigade na sojojin Najeriya, Birgediya-Janar M. A. Sadiq, ya kai masa ziyarar ban girma.

An ruwaito Idris-Ahmad yana yabawa rundunar sojin bisa wannan ziyarar, inda ya kara da cewa irin wannan hadin gwiwa zai samar da hadin kai, da magance shaye-shayen miyagun kwayoyi, laifuka da kuma tarwatsa iyali.

Hukumar, a cewarsa, tare da hadin gwiwar rundunar Sojoji, za su samar da cikakkiyar dabara don kare jihar daga illar shaye-shayen miyagun kwayoyi.

Don haka ya bukaci kungiyoyin raya kasa, masu ruwa da tsaki, al’umma da malaman addini da su marawa hukumar baya a yakin da take yi da wannan annoba.

Da yake mayar da martani, Sadiq ya yabawa hukumar bisa jajircewarta wajen yaki da shan miyagun kwayoyi.

Ya ce sun kai ziyarar ne domin hada kai da hukumar NDLEA domin magance kalubalen tsaro da ake fama da su a wannan zamani, inda ya kara da cewa, “ana tafka manyan laifuffuka ta hanyar shan miyagun kwayoyi.

“Rundunar sojin Najeriya za ta ci gaba da hada kai da hukumar ta NDLEA a kan musayar bayanan sirri, gudanar da ayyukan hadin gwiwa da kuma shirye-shirye na karfafa gwiwa don magance tushen shaye-shayen miyagun kwayoyi da hana yaduwarsa a jihar,” in ji Sadiq.

legit breaking news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp