Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce, a shirye yake ya samu nasara a kan Hamas a zirin Gaza.
Da yake magana a daidai lokacin da sabon kwamandan rundunar IDF ya soma aiki, Mista Netanyahu ya ce dole ne Isra’ila ta cimma cikakken burinta.
Janar Eyal Zamir ya ce 2025 shekarar yaƙi ce. Ya ce IDF ta samu kyawawan nasarori a fagen daga.
“Mun samu nasarori a yaƙin Gaza da Lebanon. Hamas ta fuskanci gagarumin koma-baya amma ba a kai ga yin galaba a kan ta ba,” in ji shi.
Ministan tsaron Isra’ila ya ce ƙasarsa za ta koma kai wa Hamas farmaki idan ƙungiyar ta ƙi sakin ragowar mutanen da ke tsare a hannunsu.
Isra’ila da Amurka sun yi fatali da shawarar da Masar ta bayar game da makomar Gaza inda ta ce ta gaza magance matsalolin da ake gani a Gaza.