fidelitybank

A shekara nan za mu gama da yakin Rasha – Ukraine

Date:

Shugaban ƙasar Ukraine, Volodymyr Zelensky ya bayyana cewa yana sa ran za a kawo ƙarshen yaƙin da ƙasarsa ke yi da Rasha a cikin wannan shekarar, bayan shekara uku da aka kwashe ana artabu tsakanin ɓangarorin biyu.

Zelensky ya yi wannan kalamin ne sa’ilin da manema labarai suka tambaye shi game da fatansa ga Ukraine da al’ummarta.

Muna sa ran kammala yaƙin a wannan shekarar,” in ji shi, ya ƙara da cewa ƙasar baki ɗaya “ta sha wahala.”

Sai dai ya bayyana cewa ƙasar na buƙatar samun abin da za ta dogara da shi ta fannin tsaro, domin hana Rasha sake kai mata farmaki a shekaru masu zuwa.

Ya ce shigar ƙasar cikin Tarayyar Turai da kuma ƙungiyar tsaro ta Nato nan kusa “zai taimaka ƙwarai da gaske”.

A baya-bayan nan Zelensky ya yarda cewa zai sauka daga muƙamin shugaban ƙasa idan aka amince Ukraine za ta shiga ƙungiyar Nato a madadin hakan.

Rasha ta ce ba za ta taɓa amincewa da hakan ba.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp