Shugaban ƙasar Ukraine, Volodymyr Zelensky ya bayyana cewa yana sa ran za a kawo ƙarshen yaƙin da ƙasarsa ke yi da Rasha a cikin wannan shekarar, bayan shekara uku da aka kwashe ana artabu tsakanin ɓangarorin biyu.
Zelensky ya yi wannan kalamin ne sa’ilin da manema labarai suka tambaye shi game da fatansa ga Ukraine da al’ummarta.
Muna sa ran kammala yaƙin a wannan shekarar,” in ji shi, ya ƙara da cewa ƙasar baki ɗaya “ta sha wahala.”
Sai dai ya bayyana cewa ƙasar na buƙatar samun abin da za ta dogara da shi ta fannin tsaro, domin hana Rasha sake kai mata farmaki a shekaru masu zuwa.
Ya ce shigar ƙasar cikin Tarayyar Turai da kuma ƙungiyar tsaro ta Nato nan kusa “zai taimaka ƙwarai da gaske”.
A baya-bayan nan Zelensky ya yarda cewa zai sauka daga muƙamin shugaban ƙasa idan aka amince Ukraine za ta shiga ƙungiyar Nato a madadin hakan.
Rasha ta ce ba za ta taɓa amincewa da hakan ba.