Tsohon gwamnan jihar Anambra, kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Peter Obi ya koka kan halin da tattalin arzikin Najeriya ke ciki da kuma rashin tsaro a Najeriya.
Don haka ya yi alkawarin sake daukaka Najeriya har na tsawon shekaru hudu idan aka ba shi damar mulkin kasar.
Obi ya bayyana haka ne a shelkwatar jam’iyyar PDP ta Abia da ke Umuahia, a ranar Alhamis a lokacin da ya ziyarci jihar Abia, domin neman goyon bayan wakilan Abia kan muradin sa na shugaban kasa.
Obi, wanda ya zayyana tsare-tsaren sa ga Najeriya idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa, ya ce, yana nan a fafutukar sake fasalin Najeriya domin daukakar ‘yan kasa.
Ya yi alkawarin cewa, nan da shekaru hudu kacal Najeriya za ta samu wani matsayi mai kishin kasa a kowane fanni, idan har ya samu nasarar zama shugaban kasa, ya mai da Najeriya a matsayin mai noma, ba kawai mai amfani da kayayyaki ba.