fidelitybank

A samar mana da ‘Yan sandan jihohi – Gwamnonin Arewa

Date:

Gwamnonin jihohin Arewa 19 da sarakunan gargajiya, sun yi kira da a yi garambawul ga kundin tsarin mulki na 1999, don samar da yan sandan jihohi.

A cewarsu wannan ne kadai zai sa a shawo kan matsalar tsaro da yankin ke fama da ita dama kasa baki daya.

Yankin Arewacin na Najeriya ya jima yana fama da matsalar yan fashin daji, da satar mutane don neman kudin fansa, da sauran nau’o’in ayyukan ta’addanci.

Kungiyar gwamnonin arewa ta NGF, da ta sarakunan gargajiya (NTRC) sun aminta da hakan ne bayan kammala wani taro ranar Litinin a Abuja.

Wannan ne karon farko da kungiyoyin biyu suka cimma matsayar samar da yan sandan jihohi a taron hadin gwuiwa.

Sai dai akwai masu fargabar cewa wasu gwamnonin jihohin kan iya amfani da yan sandan da za a samar a karkashin ikonsu, don cin zarafin abokan adawa ko kuma cimma burinsu na siyasa.

An dade ana kiraye-kirayen samar da yan sandan jihohi, inda masu bukatar a yi hakan ke kafa hujjar cewa rundunar yan sanda ta kasa ta yi kadan, idan aka yi la’akari da girman matsalar tsaron da kasar ke fama da ita.

daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp