fidelitybank

A samar da tsaro a makarantun gwamnati – Majalisa

Date:

Majalisar wakilai ta yi kira da a samar da tsaro a fadin makarantun kasar nan domin magance tabarbarewar tsaro a kasar nan.

Matakin da majalisar ta dauka na biyo bayan amincewa da kudirin da Billy Osawaru ya gabatar a zauren majalisar a yau.

Da yake gabatar da kudirin, Osawaru ya nuna rashin jin dadinsa ta yadda dalibai ba su da kwanciyar hankali a makarantunsu, musamman a jihohin Borno da Nasarawa da Neja da Zamfara da Katsina da kuma Kaduna.

Dan majalisar ya ce, wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wasu dalibai kusan 24 na Jami’ar Tarayya ta Gusau a Jihar Zamfara.

Ya yi gargadin cewa za a iya rufe makarantu idan har aka ci gaba da kai hare-haren ta’addanci a makarantun kasar nan.

Dan majalisar ya kara da cewa a Najeriya ‘yan sanda ba sa gadin mafi akasarin makarantun duk da irin hare-haren da makarantun ke yawan fuskanta da kuma wadanda ake da su ba su wadatar da ma’aikata da kayan aiki ba, domin haka a duk lokacin da irin wadannan hare-hare suka afku kama ya yi su dauki mataki.

Osawaeu ya kuma ce, an kashe dalibai sama da 180, sannan kusan 90 sun jikkata a hare-hare 70 tsakanin watan Afrilun 2014 zuwa Disamba 2022, inda aka yi garkuwa da ma’aikatan makarantar kusan 60 sannan aka kashe 14. An kuma lalata gine-ginen makarantu 25 a wannan lokacin.

An yi garkuwa da kimanin ‘yan makaranta 287 daga wata makaranta mallakar gwamnati a garin Kuriga na jihar Kaduna.

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp