fidelitybank

A samar da hanyoyin jin ƙai a zirin Gaza – Ƙungiyar Tarayyar Turai

Date:

Shugabannin Tarayyar Turai sun yi kiran a samar da “hanyoyin jin ƙai kuma a tsahirta” don ba da damar kai kayan agaji ga fararen hula a Gaza.

A cikin wani ƙuduri da suka ayyana yayin wani taro a Brussels, shugabannin ƙasashen Tarayyar Turai 27 sun bayyana “matuƙar damuwa saboda ƙazancewar al’amura a Gaza”.

Sun yi kira a “ci gaba kuma cikin hanzari a samar da amintacciyar hanyar jin kan ɗan’adam don kai kayan agaji ga waɗanda ke cikin tsananin buƙata ta hanyar ɗaukar dukkan matakan da suka wajaba ciki har da kafofin jin kai sannan a dakata don buƙatun ayyukan jin kai”.

Kudurin ya kuma ce Majalisar Turai “ta jaddada yin alla-wadai cikin murya mafi kaushi ga Hamas saboda hare-harenta na mugunta da ta’addanci a kan Isra’ila”.

Ta kuma kara da cewa: “Amfani da fararen hula a matsayin garkuwa da Hamas ke yi shi ma musamman aika-aika ne da ake yin tur da ita.”

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp