fidelitybank

A sako mana Jagororin mu da aka kama – Masu Zanga-zangar Katsina

Date:

Ƙungiyoyin da suka shirya zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a jihar Katsina na ta kiraye-kirayen sako jagororinsu, bayan da suka zargi jami’an tsaro da tsare su.

“Jami’an tsaron ne suka gayyaci jagororinmu domin su amsa wasu tambayoyi, sai dai tun bayan zuwansu sai aka tsare su, bisa zargin zuga wasu da ake zargi da aikata ba daidai ba a lokacin zanga-zangar,” in ji ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida yadda aka kama jagororin zanga-zangar.

Ya ce mutanen da jami’an tsaron ke tsare da su sun haɗa da: Shugaban ƙungiyar ‘Struggle for Good Governance’, Habibu Muktar Ruma, da sakataren ƙungiyar ‘Coalition for Civil Society’, Kwamared Kabiru Shehu ‘Yanɗaki.

A lokacin zanga-zangar dai a wasu wurare musamman arewacin Najeriya an samu matsalolin fashe-fashen wurare da sace-sace da lalata dukiyoyi.

To sai dai waɗannan ƙungiyoyin sun nesanta kansu daga hakan. ”Mun rubuta musu cewa za mu yi zanga-zanga daga ƙarfe 8:00 na safe zuwa 10:00 na safe, kuma da rakiyar jami’an tsaro muka yi zanga-zangarmu, har muka ƙare su ne suka ba mu kariya”, in ji shi.

”Kuma koda muka ƙare, sai da muka kira shi jagoran hukumar DSS na jihar muka sanar masa cewa ga shi mun tashi daga zanga-zangar kamar yadda muka aiko musu a rubuce, kuma ya tabbatar mana cewa yaransa ma sun shaida masa haka”.

Ya bayyana cewa bayan sun kammala ta ne wasu ɓata-gari da ke iƙirarin zanga-zangar suka je suka aikata abin da bai dace ba.

Jihar Katsina na daga cikin jihohin da suka sanya dokar taƙaita zirga-zirga, sakamakon fargabar ɓarkewar rikici a lokacin zanga-zangar da aka fara a ranar Alhamis.

latest news in nigeria today 2022 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp