fidelitybank

A sako mana Jagororin mu da aka kama – Masu Zanga-zangar Katsina

Date:

Ƙungiyoyin da suka shirya zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a jihar Katsina na ta kiraye-kirayen sako jagororinsu, bayan da suka zargi jami’an tsaro da tsare su.

“Jami’an tsaron ne suka gayyaci jagororinmu domin su amsa wasu tambayoyi, sai dai tun bayan zuwansu sai aka tsare su, bisa zargin zuga wasu da ake zargi da aikata ba daidai ba a lokacin zanga-zangar,” in ji ɗaya daga cikin waɗanda suka shaida yadda aka kama jagororin zanga-zangar.

Ya ce mutanen da jami’an tsaron ke tsare da su sun haɗa da: Shugaban ƙungiyar ‘Struggle for Good Governance’, Habibu Muktar Ruma, da sakataren ƙungiyar ‘Coalition for Civil Society’, Kwamared Kabiru Shehu ‘Yanɗaki.

A lokacin zanga-zangar dai a wasu wurare musamman arewacin Najeriya an samu matsalolin fashe-fashen wurare da sace-sace da lalata dukiyoyi.

To sai dai waɗannan ƙungiyoyin sun nesanta kansu daga hakan. ”Mun rubuta musu cewa za mu yi zanga-zanga daga ƙarfe 8:00 na safe zuwa 10:00 na safe, kuma da rakiyar jami’an tsaro muka yi zanga-zangarmu, har muka ƙare su ne suka ba mu kariya”, in ji shi.

”Kuma koda muka ƙare, sai da muka kira shi jagoran hukumar DSS na jihar muka sanar masa cewa ga shi mun tashi daga zanga-zangar kamar yadda muka aiko musu a rubuce, kuma ya tabbatar mana cewa yaransa ma sun shaida masa haka”.

Ya bayyana cewa bayan sun kammala ta ne wasu ɓata-gari da ke iƙirarin zanga-zangar suka je suka aikata abin da bai dace ba.

Jihar Katsina na daga cikin jihohin da suka sanya dokar taƙaita zirga-zirga, sakamakon fargabar ɓarkewar rikici a lokacin zanga-zangar da aka fara a ranar Alhamis.

nigeria 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp