fidelitybank

A rage lantarkin da ake baiwa kasashen makwabtakan Najeriya – NERC

Date:

Hukumar kula da wutar lantarki ta Najeriya (NERC) ta umarci kamfanin samar da wutar lantarki na ƙasar ya rage lantarkin da yake bai wa ƙasashe maƙwafta domin bunƙasa samar da wutar lantarki a cikin gida.

A cikin wata takardar umarni da hukumar ta fitar a ranar Juma’ar da ta gabata, ta ce tsarin da kamfanin samar da wutar lantarki ga ƙasashen ƙetare ke bi a halin yanzu ya jawo jefa ‘yan Najeriya cikin wahala.

Hukumar ta ƙayyade cewa kashi 6 cikin 100 na wutar da ake samarwa ne kawai za a fitar da su ƙasashen ƙetare na tsawon watanni shida masu zuwa, daga ranar 1 ga Mayu.

Akwai yarjeniyoyi da Najeriya ta ƙulla na samar da wutar lantarki ga ƙasashen Afirka da ke makwabtaka ita.

Ana yawan samun katsewar wutar lantarki a Najeriya saboda karancin wutar amma abin ya ƙara kamari a ‘yan kwanakin nan.

A baya-bayan nan ne kamfanonin samar da wutar lantarki suka ƙara kuɗin lantarki ga wasu kwastomomin cikin gida da ke samun wutar lantarki na tsawon sa’o’i 20 a kullum.

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp