Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ce, Najeriya na ci gaba ba tare da la’akari da masu sukar manufofinsa na tattalin arziki ba.
Tinubu ya bayyana hakan ne a lokacin da yake tattaunawa da manema labarai a ranar Litinin daga Legas.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban kasar ya jaddada cewa kasar na kan hanyar farfadowa duk da matsalar tattalin arziki.
Da yake magana kan kudirin kasafin kudin na shekarar 2025 na Naira tiriliyan 49.7, ya nanata hakan wani maido da fata ne.
Ya yi kira da a samu fahimtar juna da hadin kai daga ‘yan Najeriya a daidai lokacin da tattalin arzikin kasar ke ci gaba da tabarbarewa.
“Najeriya na ci gaba ba tare da la’akari da masu suka ba. Wannan kasafin kudi ne na maido da fata, kuma Najeriya na kan hanyar farfadowa. Ba za mu iya kammala aikin a cikin shekara guda ba, ”in ji shi.
Tun da farko dai Tinubu ya ce, bai yi nadamar cire tallafin man fetur ba a watan Mayun 2023.