Kungiyar Tarayyar Afrika ta ce, ta damu rahotannin nuna wariya da a ke nunawa ƴan Afirka a Ukraine a yayin da suke ƙoƙarin tsere wa yaƙi a ƙasar.
Ƙungiyar ta yi kira ga dukkanin ƙasashen da abin ya shafa su mutunta dokokin duniya tare da bayar da agaji ba tare da nuna wariya ba.
“Rahotannin wariya ga ƴan Afrika abu ne da ba za a amince ba kuma wariya ce da saɓa dokokin duniya,” kamar yadda ƙungiyar ta bayyana a cikin wata sanarwa.
Ƙungiyar ta yaba wa mambobinta da ofisoshin jekadancinsu a ƙasashen da ke makwabtaka da Ukraine kan yadda suke taimakawa mutanen da ke gujewa yaƙi.