‘Yan Afirka da ke kokarin tsere wa daga Ukraine na ƙorafin fuskantar wariya a kan iyakokin Ukraine zuwa cikin Tarayyar Turai.
Wata daliba ƴar Najeriya da ke karatun likitancia wata jami’a a Kharkiv, ta ce yi tafiya na tsawon sa’a 11 cikin dare kafin ta isa Medyka-Shehyni, da ke kan iyaka da Poland.
“Lokacin da na zo nan na ga baƙaƙen fata suna bacci kan titi,” kamar yadda ta shaida wa wakiliyar BBC.
Ta ce jami’an tsaron kan iyaka sun shaida mata cewa ta jira har dai ƴan Ukraine sun wuce sannan. Ba ta iya tantance ko masu gadin kan iyakar na Ukraine ne ko kuma Poland.
Ta ce ta ga an cika motocin bas da mutane waɗanda ta bayyana fararen fata, da aka amince su tsallaka kan iyaka, yayin da kuma ake zaɓen baƙaƙen fata da suka yi layi suna jiran tsammani.
Ruqayya na ƙoƙarin shiga Warsaw ne domin samun jirgin da zai dawo da ita gida Najeriya.
Isaac ya ce, ya wuraren ƙarfe 4.30 na safe ya isa kan iyakar Medyba kuma ya ce an faɗa masa cewa sai ƴan Ukraine da ƴan Turkiya sun wuce kafin baƙaƙen fata.
Jami’an kula da kan iyakokin Poland sun ce suna barin duk wanda ya fito daga Ukraine shiga ƙasar.
Ofishin jakadancin Najeriya a Poland ya ce, ya tura jami’ansa zuwa kan iyakoki, domin taimakawa ƴan ƙasar tsallakawa.