fidelitybank

A na nuna mana wariyar kalar fata a kan iyakar Ukraine – ‘Yan Afrika

Date:

‘Yan Afirka da ke kokarin tsere wa daga Ukraine na ƙorafin fuskantar wariya a kan iyakokin Ukraine zuwa cikin Tarayyar Turai.

Wata daliba ƴar Najeriya da ke karatun likitancia wata jami’a a Kharkiv, ta ce yi tafiya na tsawon sa’a 11 cikin dare kafin ta isa Medyka-Shehyni, da ke kan iyaka da Poland.

“Lokacin da na zo nan na ga baƙaƙen fata suna bacci kan titi,” kamar yadda ta shaida wa wakiliyar BBC.

Ta ce jami’an tsaron kan iyaka sun shaida mata cewa ta jira har dai ƴan Ukraine sun wuce sannan. Ba ta iya tantance ko masu gadin kan iyakar na Ukraine ne ko kuma Poland.

Ta ce ta ga an cika motocin bas da mutane waɗanda ta bayyana fararen fata, da aka amince su tsallaka kan iyaka, yayin da kuma ake zaɓen baƙaƙen fata da suka yi layi suna jiran tsammani.

Ruqayya na ƙoƙarin shiga Warsaw ne domin samun jirgin da zai dawo da ita gida Najeriya.

Isaac ya ce, ya wuraren ƙarfe 4.30 na safe ya isa kan iyakar Medyba kuma ya ce an faɗa masa cewa sai ƴan Ukraine da ƴan Turkiya sun wuce kafin baƙaƙen fata.

Jami’an kula da kan iyakokin Poland sun ce suna barin duk wanda ya fito daga Ukraine shiga ƙasar.

Ofishin jakadancin Najeriya a Poland ya ce, ya tura jami’ansa zuwa kan iyakoki, domin taimakawa ƴan ƙasar tsallakawa.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp