fidelitybank

A na lugudan wuta a ƙasar Sudan

Date:

An samu arangama mai ƙarfi tsakanin dakarun sojin Sudan da rundunar mayaƙan RSF, a kusa da sansanin soji da ke birnin Khartoum na ƙasar Sudan.

Cikin wata sanarwa da sojojin suka wallafa a shafinsu na Facebook ranar talata da daddare, sun ce sun daƙile wani hari da RSF suka kai sansanin soji da ke yankin Al-Shajara a kudancin birnin Khartoum.

Sojojin sun kuma yi iƙirarin kashe da yawa daga cikin mayaƙan RSF ɗin.

A nata ɓangare, mayaƙan na RSF sun ce sun ƙwace iko da wasu yankuna a sansanin tare da kama makamai masu dinbim yawa, cikin wata sanarwa da suka fitar a shafinsu na X da a baya aka fi sani da Twitter.

Gidan talbijin na Al Arabiyya – da ƙasar Saudiyya ke ɗaukar nauyinsa – ya ce har yanzu sojojin ne ke iko da sansanin bayan kwashe kwana uku ana gwabza faɗa a sansanin.

A ‘yan kwanakin nan faɗa na ci gaba da rincaɓewa a birnin Khartoum da biranen Omdurman da Bahri da wasu yankunan yankin Darfur.

Majalisar Dikin Duniya ta ce dubban mutane ne suka mutu, yayin da aka raba da sama da mutum miliyan huɗu da muhallansu tun bayan ɓarkewar yaƙi tsakanin sojoji da dakarun RSF a tsakiyar watan Afrilu

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp