Yau ne za a kammala zaɓukan da aka gaza samun gwani a cikinsu, a rumfunan zaɓe 69 a faɗin jihar Adamawa a zaɓen gwamnan da aka fafata a watan jiya.
Rikci da aka samu ya sanya Hukumar Zaɓe mai zaman kanta INEC ta ayyana zaɓen a matsayin wanda bai kammala ba.
Ya kamata a fara zaɓe da misalin ƙarfe 8 na safe a ƙauyen Ajiya da ke makwabtaka da Yola, gwamman mutane sun yi zaman jira na kimanin awa ɗaya domin su kaɗa kuri’arsu.
Zaɓen da aka yi a ranar 18 ga watan Maris cike yake da zargin an yi maguɗi, kuma duka ɓangarorin biyu na gwamna mai ci na jam’iyyar PDP da na jam’iyyar adawa ta APC duk sun yi wannan iƙirari.
A sakamakon zaɓen da INEC ta bayyana a baya, gwamna mai ci Ahmadu Fintiri ne ke kan gaba da ƙuri’u 421,524 yayin da Sanata Aishatu Dahiru Binani take da 390,275.
Ƙuri’a 31,249 ce ke tsakanin ‘yan takarar biyu.
Idan Aisha Binani ta yi nasara za ta zama zaɓaɓɓiyar gwamna mace ta farko a Najeriya.