Za a gudanar da wata addu’a ta mausamman ga Najeriya yau Juma’a a babban masallacin ƙasa da ke Abuja, a matsayin wani ɓangare na murnar cikar shugaban ƙasar shekara 73 da haihuwa.
Fadar shugaban ƙasar ce ta sanar da haka a cikin wata sanarwa da mai bashi shawara kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga ya fitar.
Sanarwar ta ce Tinubu zai haɗu da al’umma Musulmi a massalacin a yau Juma’a domin addu’ar, domin zagayowar ranar haihuwarsa wadda za ta kasance gobe Asabar 29 ga watan Maris.
Sanarwar ta ce za a yi amfani da damar wajen yin godiya ga Allah da ya ba shi tsawon rai kuma yake taimakasa gudanar da gagarumin aikin jagorantar Najeriya.
Sanarwar ta ce shugaba “Tinubu ya yi imanin cewa gabatar da addu’o’i a matsayin ƙasa ɗaya wani babban abu ne dai zai taimaka wajen kai ƙasar ga ci gaba da zaman lafiya.”
Tinubu ya kuma buƙaci ɗaukacin al’ummar musulmi su yi addu’oi’n ga ƙasar a duk inda suke.
Shugaban ƙasar ya kuma miƙa godiyarsa ga ƴan Najeriya bisa goyon bayan da suke ba gwamnatinsa a ƙoƙarin da yake yi ba dare ba rana wajen bunƙasa tattalin arziƙi da inganta tsaro da kuma faɗaɗa samun damarmaki ga ƴan ƙasar.
Ya ce ” ina matuƙar godiya ga Allah na rayuwar da ya ba ni damar hidimtawa Najeriya. A yayin da nake murnar zagoyowar ranar haihuwata, zuciyata a cike take da sabuwar fata ga Najeriya. Ina buƙatar ƴan Najeriya su yi addu’a, da haɗin kansu zamu shawo kan matsalolinmu kuma mu gina ƙasar da kowa zai amfana’.”
Tinubu ya kawo sauye-sauye da dama a ɓangaren tattalin arziƙin ƙasar tun bayan hawan sa kan mulki a shekara 2023, sai dai al’ummar ƙasar na kokawa kan yadda tsare-tsaren gwamnatin ke jefa su cikin ƙunci, sanadiyyar tashin farashin kayan masarufi da kuma talauci