fidelitybank

A na fuskantar yanayi na yaki – Sojoji

Date:

Shalkwatar tsaro ta bayyana hare-haren bam na baya-bayan nan da aka kai jihar Borno a matsayin wani yanayi da ya mayar da ƙasar cikin yanayin yaƙi.

Bayanin hakan na ƙunshe cikin wata sanarwar da daraktan yaɗa labarai na hedikwatar tsaron, Manjo Janar Edward Buba ya fitar ranar Talata.

Manjo Janar Buba ya bayyana cewa hari na farko a ranar Asabar ya faru da ƙarfe 3:00 na rana lokacin da wata ƴar ƙunar baƙin wake da ta yi bad-da-kama a matsayin mabaraciya ta durfafi wani wajen biki a unguwar Mararaba Hausari tare da ta da abin fashewa.

Sai dai bayan nan da ƙarfe 5 na yammacin ranar yayin da ake ƙoƙarin kwashe mutanen da suka jikkata sakamakon harin farko zuwa asibiti domin samun kulawa, aka sake samun wata da ta sake ta da abin fashewa kusa da inda lamarin farko ya afku.

A cewar Buba, sojoji nan da nan suka ayyana dokar hana fita a garin domin hana zirga-zirga.

Sai dai a yayin da sojojin da sauran jami’an tsaro ke tabbatar da dokar hana fitar ne kuma aka sake samun wani abin fashewar da ya tashi.

Ya ce “Hari na uku ya shafi sojoji da ke koƙarin tabbatar da dokar hana fita. Wata matar ce kuma ta kai harin lamarin da ya halaka soji guda da kuma wasu jami’an tsaro biyu.

“Hari na huɗu kuma, an daƙile shi lokacin da wadda ake zargi ta ta da bom da ya yi ajalinta. A jumulla, mutum 20 ne suka mutu yayin da 52 suka ji rauni kma suna jinya a asibiti.” in ji sanarwar.

Hedikwatar tsaron ta ƙara da cewa mayaƙan sun kai hare-haren ne kan mutanen da ba su ji ba su gani ba domin nuna cewa suna nan da ƙarfinsu.

“Rundunar soji tana sane da cewa mayaƙan na son karkato da hankali gare su, su kuma rage goyon bayan da ake bai wa sojoji da kuma gwamnati.”

Kan haka ne rundunar ta yi kira ga al’umma da su ci gba da haɗa kai su kuma yi taka tsan-tsan tare da ƙara tallafa wa ƙoƙarin dakarun ƙasar domin tabbatar da tsaron rayuka a ƙasar.

daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp