fidelitybank

A na fuskantar barkewar Ebola a Najeriya

Date:

Hukumomi sun ce kasar nan na fuskantar barazanar barkewar cutar Ebola, da ake tunanin shigo da ita daga kasar Uganda.

Hukumar dakile cutuka masu yaduwa ta kasar NCDC ta ce an samu karuwar baranazar barkewar cutar ne sakamakon yawan zirga-zirgar fasinjoji da aka yi tsakanin Najeriya da Uganda, da kuma cudanyar fasinjoji, musamman a filayen jiragen sama na Nairobi, da na Addis Ababa, da kuma filin jirgin sama na Kigali.

Hukumomin lafiyar kasar sun ce suna cikin shirin ko ta kwana, yayin da suka dauki matakan da suka dace domin yakar cutar idan ta barke.

Matakan sun hada da sanya ido kan fasinjoji tare da tantance su a filayen jiragen saman kasar.

Hukumar ta shawarci ‘yan kasar da su guji yin tafiye-tafiye zuwa Uganda idan ba ta zama dole ba, daga yanzu zuwa wasu lokuta.

NCDC ta ce fasinjojin da suka zo kasar daga Uganda za a sanya ido a kansu na tsawon mako uku, domin tabbatar da halin da suke ciki.

An samu bullar cutar a kan mutum 100 tare da mutuwar mutum 30 a Uganda, tun bayan barkewarta a watan Satumba, ana kuma fargabar cewa cutar ka iya yaduwa zuwa makwabtan kasashe.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya baiwa ‘yan wasan kwallon kwando dala dubu 100 da filaye a Abuja

Gwamnatin Tarayya ta karrama kungiyar kwallon kwando ta mata...

‘Yan siyasa na kara matsin lamba Jonathan ya fito takara a 2027 – Bashir

Tsohon mai taimaka wa tsohon shugaban kasa kan harkokin...

Gwamnati ta karbi tawagar ‘yan wasan kwallon kwando D’Tigress

Tawagar ƴan wasan ƙwallon kwando mata ta Najeriya ta...

Na ki marawa Atiku baya ne saboda juyin yankin Kudu ne – Wike

Ministan babban birnin tarayya (FCT), Nyesom Wike, a wata...

An saki sakamakon jarabawar WASSCE

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma ta fitar da...

Sojojin Isra’ila sun kashe Falasdinawa wajen karbar abinci

Rahotanni daga Gaza na cewa sojojin Isra'ila sun sake...

Ambaliya ya shanye jihohin Bauchi da Filato da kuma Neja

Ambaliya ta cinye gonaki da gidaje da makarantu da...

Najeriya ta lashe gasar kwallon kwandon Afrika

Tawagar Æ´an wasan kwando na matan Najeriya ta lashe...

Obi ba zai iya lashe zabe a yankin Arewa ba – Keyamo

Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo, ya ce É—aya...

Iya wa’adi daya ya ishe ni a mulkin Najeriya – Peter Obi

Tsohon É—an takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar Labour, Peter...

Luis Diaz ya zaba wa kansa makoma da ya bar Liverpool – James

Kyaftin din Colombia, James Rodríguez, ya dage cewa dan...

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu...
X whatsapp