Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban ƴansanda na birnin Ahmedabad na cewa akwai yiwuwar babu wanda ya tsira da ransa a hatsarin da jirgin sama mallakin kamfanin sufuri na India Air ya samu yau a birnin.
Ya bayyana hakan ne yayin da bayani ke ƙara fitowa kan hatsarin jirgin da ke kan hanyarsa ta zuwa birnin London na ƙasar Birtaniya.
Jirgin ya faɗa kan wata unguwa jim kadan barin tashi daga filin jirgin Ahmedabad da ke yammacin ƙasar Indiya.
A lokacin da yake jawabi, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin ƙasashen waje ta Najeriya, Randhir Jaiswal ya bayyana hatsarin jirgin a matsayin “babban abin jimami”.
“Ana ci gaba da aikin ceto. Za mu tsaya tukuna domin samun ciakken bayani game da hatsarin,” in ji shi.
Sai dai ya ƙara da cewa: “Mun yi asarar mutane da dama.”