Turmutsutsu ya barke a lokacin da ake gudanar da rabon zakka ga talakawa a jihar Bauchi ya yi sanadiyar mutuwar mutane hudu.
Rikicin ya afku ne da misalin karfe 10 na safe a hedikwatar kamfanin Shafa Holdings Plc da ke kan titin Jos, a ranar Lahadi.
Wata yarinya ‘yar shekara 17 mai suna Naima Abdullahi, yanzu haka tana jinya a asibitin koyarwa na jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Ahmed Wakili, ya ce an daidaita lamarin har ya zuwa lokacin mika rahotonsa.
Wakili ya ce ‘yan sandan sun yi gaggawar daukar matakin ne da jin labarin, inda ya kara da cewa kwamishinan ‘yan sandan ya karfafa wa jama’a gwiwa da su yi hakuri.