Hukumomi a ƙasar Guinea na neman yin wata doka da za ta bai wa hukumomi damar kula da shafukan sada zumunta domin kare ƙananan yara daga ganin abubuwa masu cutarwa a shafukan.
Firaministan ƙasar, Amadou Oury-Bah ya bai wa ma’aikatar kula da kamfanonin sadarwa da ma’aikatar sadarwar ƙasar umarnin lalubo ƙudirin dokokin domin taƙaita wa yara abubuwan da za su riƙa gani a shafukan.
Ya ce matakin zai taimaka wa iyayen yara wajen kula da abubuwan da yaran nasu za su riƙa gani a shafukan na sada zumunta.
Mista Oury-Bah ya ce sabuwar dokar za ta taƙaita wa yaran ganin abubuwan da ya kira ‘marasa dacewa’ da ake wallafawa a shafukan.
Wannan doka idan ta tabbata za ta kasance mafi tsauri da aka ƙaƙaba wa shafukan sada zumunta a Afirka.
To sai dai masu suka na ganin matakin wani shirin gwamnati ne ta taƙaika wa al’ummar samun bayanai a ƙasar da ke da tarihin cusgunawa wa kafafen yaɗa labarai, ƙarƙashin mulkin sojoji