Hukumar gyaran hali ta Najeriya (NCoS) ta ce, ta ƙaddamar da bincike tare da farauta mai zurfi domin kama fursunoni bakwai da suka tsere daga gidan gyaran hali da ke Ilesa a Jihar Osun, bayan ruwan sama mai ƙarfi da ya lalata tsaron wurin.
Mai magana da yawun hukumar, Umar Abubakar, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar da daren Talata.
Lamarin ya faru da misalin ƙarfe 2 na dare, a ranar Talata, 20 ga watan Mayun 2025, inda hakan ya haifar da tserewar fursunoni bakwai.
“Biyo bayan faruwar lamarin, shugaban hukumar gyaran hali na ƙasa, Sylvester Ndidi Nwakuche, ya bayar da umarnin gaggauta gudanar da bincike kan yadda fursunonin suka samu damar tserewa,” in ji sanarwar.
Sanarwar ta ƙara da cewa hukumar tana aiki kafada da kafada da sauran hukumomin tsaro da shugabannin al’umma domin kamo waɗanda suka tsere tare da mayar da su gidan yari.
Hukumar ta kuma nemi haɗin kai da goyon bayan jama’a wajen bayar da duk wata bayani da zai iya taimakawa wajen kamo waɗanda suka tsere.