fidelitybank

A na cigaba da farautar Fursunonin Osun da suka tsere

Date:

Hukumar gyaran hali ta Najeriya (NCoS) ta ce, ta ƙaddamar da bincike tare da farauta mai zurfi domin kama fursunoni bakwai da suka tsere daga gidan gyaran hali da ke Ilesa a Jihar Osun, bayan ruwan sama mai ƙarfi da ya lalata tsaron wurin.

Mai magana da yawun hukumar, Umar Abubakar, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar da daren Talata.

Lamarin ya faru da misalin ƙarfe 2 na dare, a ranar Talata, 20 ga watan Mayun 2025, inda hakan ya haifar da tserewar fursunoni bakwai.

“Biyo bayan faruwar lamarin, shugaban hukumar gyaran hali na ƙasa, Sylvester Ndidi Nwakuche, ya bayar da umarnin gaggauta gudanar da bincike kan yadda fursunonin suka samu damar tserewa,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta ƙara da cewa hukumar tana aiki kafada da kafada da sauran hukumomin tsaro da shugabannin al’umma domin kamo waɗanda suka tsere tare da mayar da su gidan yari.

Hukumar ta kuma nemi haɗin kai da goyon bayan jama’a wajen bayar da duk wata bayani da zai iya taimakawa wajen kamo waɗanda suka tsere.

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp