fidelitybank

A na cigaba da aikin ceto Gawarwakin da suka nutse a kogin Neja

Date:

Hukumomi a jihar Neja na ci gaba da gudanar da bincike kan sauran gawarwakin da ake tsammanin har yanzu suna cikin ruwan da wani kwale-kwale ya kife a ranar Lahadi.

Haɗarin ya faru ne a yankin Gbajibo na Ƙaramar Hukumar Mokwa a jihar Neja da ke arewacin Najeriya.

Malam Jibrin Abdullahi Murege shi ne Shugaban Ƙaramar Hukumar ta Mokwa wanda ya ce ya zuwa yanzu mutum 26 sun mutu, yayin da aka ceto sama da mutum 40, cikin kimanin mutum 100 da ke cikin jirgin.

Mahukunta sun ce mata manoma da yara ƙanana ne kawai a cikin jirgin, kuma suna ci gaba da gudanar da bincike domin tabbatar da an gano yawan adadin mutanen da rahotanni suka ce suna cikin jirgin.

Haɗarin jirgin ya faru ne sakamakon wani ice da jirgin ya daka a tsakiyar ruwa, wanda mahukunta suka ce an yanke shi ne a baya amma damuna ta sa ya ƙara toho kuma ba a iya ganinsa.

Kifewar jirgin ruwa a jihar Neja ba baƙon abu ba ne, ko wata uku baya sai da aka samu irin wannan kifewar jirgi mai ɗauke da mutane sama da 100 da suke kan hanyarsu ta dawowa daga gidan biki.

A wani labarin mai kama da wannan, wani jirgin ruwan ya kife a jihar Adamawa da ke arewa maso gabashin Najeriya ɗauke da mutum 23 a ranar Juma’a.

Rahotanni sun ce mutum 15 sun mutu waɗanda yawancin su manoma ne da ‘yan kasuwa da ke tare da ƙananan yara.

Haɗarin ya faru ne a kan hanyarsu ta zuwa birnin Yola daga ƙauyen Rugange da ke Ƙaramar Hukumar Yola ta Kudu.

An gano gawarwaki huɗu a lokacin da abin ya faru, sanadin masu aikin ceto da kuma masu ninƙaya na gargajiya.

Wani wanda abin ya faru a kan idanunsa ya ce, wata iska ce mai ƙarfi ta janyo faɗuwar jirgin.

www.najnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp