fidelitybank

A na bincike kan tsige kan wani Almajiri da wuka a Kano

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta fara gudanar da bincike kan halin da ake ciki dangane da zargin fille kan wani karamin yaro Mohammed Saidu da wani Almajiri ya yi a kauyen Kanwa da ke karamar hukumar Madobi a jihar.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Usaini Gumel, ya shaida wa manema labarai ranar Juma’a a Kano cewa, almajiri mai shekaru 16 da haihuwa, mai suna Abdullahi ne ya kashe Saidu mai shekaru 6.

Ya ce Abdullahi, wanda dan Zamfara ne, wani ne ya hango shi a kauyen Kanwa a lokacin da yake rike da wuka mai dauke da jini da ake zargin jinin mutum ne.

Ya ce an tsinci gawar Saidu marar kai a wata makarantar firamare da ke kusa.

A cewarsa, daga nan ne aka kai wanda ake zargin zuwa gidan hakimin kauyen don hana a kashe shi.

Ya ce ’yan gari da suka fusata, sun mamaye kauyen, inda suka gangaro kan wanda ake zargin, suka kuma yi masa munanan raunuka.

Ya ce a lokacin da ‘yan sandan suka isa wurin, wanda ake zargin ya amsa laifinsa, inda ya ce ya jefar da wanda aka kashen ne a cikin wani rami na bayan gida da ke kusa da makarantar firamare.

Ya ce an kai wanda ake zargin zuwa asibitin Kwankwaso Cottage Hospital amma ya mutu a lokacin da ake jinya.

Shugaban ‘yan sandan jihar ya ce, an tsinto gawar mamacin kuma an garzaya da su asibiti domin a duba su, daga bisani kuma aka mika su ga ‘yan uwansa domin yi musu jana’iza.

legit nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp