Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta fara gudanar da bincike kan halin da ake ciki dangane da zargin fille kan wani karamin yaro Mohammed Saidu da wani Almajiri ya yi a kauyen Kanwa da ke karamar hukumar Madobi a jihar.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Usaini Gumel, ya shaida wa manema labarai ranar Juma’a a Kano cewa, almajiri mai shekaru 16 da haihuwa, mai suna Abdullahi ne ya kashe Saidu mai shekaru 6.
Ya ce Abdullahi, wanda dan Zamfara ne, wani ne ya hango shi a kauyen Kanwa a lokacin da yake rike da wuka mai dauke da jini da ake zargin jinin mutum ne.
Ya ce an tsinci gawar Saidu marar kai a wata makarantar firamare da ke kusa.
A cewarsa, daga nan ne aka kai wanda ake zargin zuwa gidan hakimin kauyen don hana a kashe shi.
Ya ce ’yan gari da suka fusata, sun mamaye kauyen, inda suka gangaro kan wanda ake zargin, suka kuma yi masa munanan raunuka.
Ya ce a lokacin da ‘yan sandan suka isa wurin, wanda ake zargin ya amsa laifinsa, inda ya ce ya jefar da wanda aka kashen ne a cikin wani rami na bayan gida da ke kusa da makarantar firamare.
Ya ce an kai wanda ake zargin zuwa asibitin Kwankwaso Cottage Hospital amma ya mutu a lokacin da ake jinya.
Shugaban ‘yan sandan jihar ya ce, an tsinto gawar mamacin kuma an garzaya da su asibiti domin a duba su, daga bisani kuma aka mika su ga ‘yan uwansa domin yi musu jana’iza.