A yau Lahadi ne za a rantsar da shugaban ƙasar Rwanda Paul Kagame a karo na huɗu.
Ya samu nasarar zaɓen da aka gudanar a watan da ya gabata da kashi 99 cikin ɗari na ƙuru’un da aka kaɗa.
Kodaya ke bai fuskanci wata hamayya mai ƙarfi ba sakamakon hana manyan jagororin hamayyar ƙasar takara.
Wakilin BBC ya ce ana yabon Kagame da samar da zaman lafiya a Rwanda tun bayan kisan ƙare-dangi na 1994.
To amma kuma ana zarginsa da take haƙƙin ƴan hamayya da kuma rura wutar rikici a maƙwabciyar ƙasar Jamhuriyar Dumokuraɗiyyar Kongo.
Za a gudanar da taron rantsuwar ne a filin wasa na Amahoro da ke babban birnin ƙasar Kigali.