fidelitybank

A na ban kwana da gawar Pele

Date:

‘Yan Brazil za su yi wa gawar fitaccen tsohon ɗan wasan duniyar nan ɗan ƙasarta Pelé girmamawar ƙarshe kafin yi masa jana’iza ranar Talata.

An ajiye gawar ɗan wasan ranar Litinin a tsakiyar filin wasa na Urbano Caldeira, wanda ya kasance filin wasan tsohuwar ƙungiyarsa ta Santos.

Dubban magoya bayan tsohon ɗan wasan sun fara bin dogayen layuka ɗauke da tutoci da hotunan tsohon ɗan ƙwallon, wanda ya lashe Kofin Duniya sau uku, dan shiga filin wasan domin yin ban kwanan ƙarshe da gawar.

Za a fara shirye-shiryen yi wa gawar tsohon ɗan wasan ranar Talata, inda za a ɗauki gawar Pele a zagaya da ita kan titunan birnin Santos, ciki har da kan titin da gidan mahaifiyarsa Celeste Arantes mai shekara 100 ke zaune.

Bayan kammala zagayawa da gawar ne kuma ‘yan uwansa za su yi masa jana’iza tare da binni shi a maƙabartar Memorial Necrópole Ecumênica cemetery.

fg spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp