fidelitybank

A na Alihinin mutuwar shugaban Bankin Access bayan jirgin sama ya hallaka shi da iyalansa a Amurka

Date:

A Najeriya manyan mutane na ci gaba da nuna alhininsu kan rasuwar shugaban bankin Access na Najeriya, Herbert Wigwe wanda ya rasu a Amurka sakamakon hatsarin jirgi mai saukar ungulu da yake ciki tare da iyalansa.

Mista Wigwe tare da matarsa da kuma ɗansa sun rasa rayukansa ne a cikin hatsarin jirgin saman mai saukar ungulu a ranar Juma’ar da ta gabata a Amurka .

Jagoran adawa Atiku Abubakar ya aike da saƙon ta’aziyyarsa ga kan rasuwar mutumin da ya bayyana da fasihin mutum mai halin kirki da dattaku.

Cikin saƙon ta’aziyyar da ya wallafa a shafnsa na X, tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya ce ya kadu matuƙa da labarin rasuwar mista Wigwe, wanda ko yaushe burinsa shi ne tunanin kawo ci gaba.

Ita ma shugabar ƙungiyar kasuwanci ta duniya, Ngozi Okonjo Iweala, ta bayyana mutuwar Mista Wigwe mai shekara 57 da matarasa da dansa a matsayin babban rashi ga Najeriya baki ɗaya.

Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani a nasa ɓangare ya bayyana marigayin da cewa ɗaya ne daga cikin mutanen da ke da fikirar ɓullo da sabbani abubuwa

Tuni dai masu bincike a California suka fara bincike kan abin da ya janyo hatsarin jirgin.

Haka kuma wasu mutane uku da ke ciki jirgin suma sun mutu yayin da jirgin ya fado a lokacin da yake kan hanyarsa ta zuwa garin Boulder daga Palm Springs a jihar Nevada.

Rahotonni na cewa an samu yanayi mara kyau tare da ruwan sama da zubar dusar ƙanƙara a yankin.

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp