Mazauna Kano, jihar da ta fi kowacce yawan al’umma a Najeriya da jihohin Jigawa da Katsina na ci gaba da kokawa kan rashin wutar lantarki.
Hakan ya biyo bayan ɗauke wutar da kamfanin rarraba wutar lantarki da ke jihar Kano (KEDCO) ke yi.
Wasu mazauna birnin sun ce wutar da suke samu bata wuce sa’oi biyu zuwa uku a kullum, a kwanaki uku da suka gabata.
Mazauna jihohin uku na daga cikin jihohin da ke fuskantar yanayi na zafi a arewacin ƙasar, lamarin da ya sa ake matuƙar buƙatar wutar don sanyaya abubuwan sha da abinci da gidaje ko shagunansu.
Hakan na zuwa ne yayin da ƙananan masana’antu ke fuskantar matsaloli sakamakon ƙarancin wutar lantarkin.
Lamarin da ya kai ga durƙushewar wasunsu tun a baya.