A wannan makon ne ake sa ran jam`iyyar APC mai mulkin Najeriya za ta gudanar da babban taronta na zabar sabbin shugabanni da za a damƙa wa ragamar jam`iyyar.
Mutum takwas ne ke takarar shugabancin jam`iyyar, duk kuwa da rahotannin da ke cewa, Shugaba Muhammadu Buhari na goyon bayan guda daga cikin su.
Masana dai na cewa, babban taron ya na da tasiri sosai a kan makomar jam`iyyar APC.
Duk da cewa, shugaban riko na jam`iyyar APC, wato gwamnan jihar Yobe, Alhaji Maimala Buni da`yan kwamitinsa na cewa, shiri ya yi nisa game da babban taron jam`iyyar na kasa, a bangaren masu neman takara za a iya cewa, ta na kasa ta na dabo ganin cewa, mutum takwas ne ke neman shugabancin jam`iyyar.