Babbar kungiyar ‘yan Jamhuriyar Nijar mazauna kasashen waje, HCNE, reshen Najeriya, ta yi kira ga shugabannin kasashen biyu su tattauna kan kisan gillar da ake yi wa ‘yan kasar a kudancin Najeriya.
A cikin wannan mako ne aka kashe wasu ‘yan Nijar bakwai a wasu garuruwa da ke Kudancin Najeriya.
Shugaban kungiyar ‘yan Nijar mazauna Najeriya, Alhaji Abubakar Khalid, ya fada wa BBC cewa biyar daga cikin wadanda aka kashen sun fito ne daga yankin Mada Runfa.
”Muna son gwamnatoci a Najeriya da Nijar su bi mana kadin wadannan mutane namu da aka kashe,” in ji shi.