A karshe tsohon gwamnan jihar Zamfara, Alhaji Abdulaziz Yari da Sanata Kabiru Garba Marafa da wasu jiga-jigan jam’iyyar APC sun sauya sheka zuwa jam’iyyar PDP.
Da yake zantawa da manema labarai a Gusau a ranar Lahadi, shugaban jam’iyyar PDP na jihar Zamfara, Kanar Bala Mande mai ritaya, ya tabbatar da cewa jam’iyyar ta karbi Yari, Marafa da sauran manyan ‘yan jam’iyyar APC da suka koma jam’iyyar tare da magoya bayansu.
Mande ya ce, “‘yan jarida mun kira ku ne domin mu yi muku bayani kan shigowar babbar jam’iyyarmu ta PDP da tsohon Gwamna, mai girma Gwamna, Alhaji Abdulaziz Yari, Sanata Kabiru Garba Marafa da magoya bayansu suka yi.
“Sun tare da mu, mun cimma yarjejeniya kuma za mu aiwatar da yarjejeniyar.