fidelitybank

A karon farko an gurfanar da Mutanen da ake zargi da kai hari Cocin Owo

Date:

Mutum biyar da ake zargi da shirya harin bam a Coci Katolika ta Saint Francis da ke Owo, Jihar Ondo, a shekarar 2022, sun musanta tuhume-tuhume tara na ta’addanci da gwamnatin Tarayya ta shigar a kansu.

An gurfanar da su a gaban Mai Shari’a Emeka Nwite na babbar kotun tarayya a ranar Litinin, inda ake zargin su da kasancewa mambobin ƙungiyar ta’addanci ta Al-Shabab a sashenta na jihar Kogi, kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.

Mai Shari’a Nwite ya sanya ranar 19 ga Agusta, 2025 a matsayin ranar fara sauraron shari’ar, sannan ya yi umarni da a ci gaba da tsare su a hannun hukumar tsaro ta DSS.

Gurfanar na zuwa ne bayan shekara uku da tsohon babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Lucky Irabor, ya sanar da cewa an kama waɗanda ake zargi da kitsa harin.

Majalisar tsaro ta ƙasa ta danganta harin da miyagun ayyukan ƙungiyar ta’addanci ta ISWAP.

Fiye da mutum 40 ne suka rasu a harin, sannan da da dama suka jikkata, lokacin da ƴanbindigar suka kai farmaki a cocin a wata ranar Lahadi a daidai lokacin da suka gudanar da ibada.

Tsohon gwamnan Jihar, marigayi Rotimi Akeredolu, ya bayyana harin a matsayin “cin zarafin ɗan’adam.”

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp