fidelitybank

A karon farko an gurfanar da Mutanen da ake zargi da kai hari Cocin Owo

Date:

Mutum biyar da ake zargi da shirya harin bam a Coci Katolika ta Saint Francis da ke Owo, Jihar Ondo, a shekarar 2022, sun musanta tuhume-tuhume tara na ta’addanci da gwamnatin Tarayya ta shigar a kansu.

An gurfanar da su a gaban Mai Shari’a Emeka Nwite na babbar kotun tarayya a ranar Litinin, inda ake zargin su da kasancewa mambobin ƙungiyar ta’addanci ta Al-Shabab a sashenta na jihar Kogi, kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.

Mai Shari’a Nwite ya sanya ranar 19 ga Agusta, 2025 a matsayin ranar fara sauraron shari’ar, sannan ya yi umarni da a ci gaba da tsare su a hannun hukumar tsaro ta DSS.

Gurfanar na zuwa ne bayan shekara uku da tsohon babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Lucky Irabor, ya sanar da cewa an kama waɗanda ake zargi da kitsa harin.

Majalisar tsaro ta ƙasa ta danganta harin da miyagun ayyukan ƙungiyar ta’addanci ta ISWAP.

Fiye da mutum 40 ne suka rasu a harin, sannan da da dama suka jikkata, lokacin da ƴanbindigar suka kai farmaki a cocin a wata ranar Lahadi a daidai lokacin da suka gudanar da ibada.

Tsohon gwamnan Jihar, marigayi Rotimi Akeredolu, ya bayyana harin a matsayin “cin zarafin ɗan’adam.”

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari a ƙauyuka 15 na Zamfara a mako ɗaya – Rahoto

Wani rahoto da tashar Channels ta ruwaito daga cibiyar Zamfara Circle...

Jihohin Arewa huɗu ne suke biyan mafi ƙarancin fansho na N32,000 – NUP

Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce...

A karon farko an gurfanar da Mutanen da ake zargi da kai hari Cocin Owo

Mutum biyar da ake zargi da shirya harin bam...

Peter Obi na nan a cikin jam’iyyar har yanzu – LP

Shugaban ƙungiyar Obidient Movement, Dr. Tanko Yunusa ya ce...

Yadda Mahara sun kashe mutum biyu, sun ƙona gidaje a Filato

Wasu da ake zargin mahara sun afka wa karamar...

An YI zanga-zanga a Isra’ila kan shirin Netanyahu na mamaye Gaza

Dubban mutane sun fito kan tituna a faɗin Isra'ila,...

Birtaniya za ta fara tisa ƙeyar bakin da suka aikata laifi zuwa kasarsu

Birtaniya ta fitar da sabon tsarin tisa keyar duk...

NDLEA ta kama Fasto kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Gwamnoni sun mika sakon ta’azziya ga iyalan Audu Ogbeh

Shugaban ƙungiyar gwamnonin arewa kuma gwamnan jihar Gombe, Muhammadu...

Duk wahala sai dai mu mutu a Gaza – Fatma

Wata mai mai ƴaƴa tara ta ce, duk runtsi...

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...
X whatsapp