fidelitybank

A karo na farko Yarima Harry da Meghan na ziyara a Najeriya

Date:

A ranar Juma’a ne yarima Harry da mai ɗakinsa Meghan Markle – masu riƙe da sarautar Duke da Duchess na Sussex na Birtaniya, ke wata ziyara ta yini uku a Najeriya.

Ma’auratan za su je Najeriya – a karon farko – bisa gayyatar da suka samu daga babban hafsan tsaron ƙsar Janar Chritopher Musa.

Ana sa rai za su kai ziyara wata cibiyar gyaran hali tare da ganawa da ƙungiyoyi da ke aiki domin tallafawa walwalar ƴan mazan jiya.

A yayin ziyarar tasu ta yini uku, za su je jihar Kaduna da ke arewa maso yammacin Najeriya domin tattaunawa da sojojin da suka ji rauni da iyalansu.

Za kuma su kai ziyara zuwa jihar Legas.

Rundunar sojin Najeriya sun ce ziyarar ta wanda ya assasa wasan Invictus da ake shiryawa domin ƴan mazan jiya da sojojin da suka ji rauni a filin daga, za ta taimaka wa sojojin da suka ji rauni sanadiyyar aiki.

Najeriya dai na neman ta karɓi baƙuncin gasar ta Invictus Games a 2029.

Meghan kuma za ta jagoranci wani taron mata a shugabanci.

Ofishin jakadancin Birtaniya a Abuja ya ce ba shi da hannu a ziyarar ta Meghan da Harry saboda ma’auratan na ziyarar ne a ƙashin kansu.

nnn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp