A karo na farko tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya hallaci taron yaye daliban da su ka yi saukar Alkur’ani mai girma a makarantar Key Special Academy dake babban birin tarraya Abuja, tare da matarsa Hajiya Salamatu Kwankwaso, a ranar Asabar.
Mutane da dama ba su taba ganin fuskar matar Kwankwaso ba, ko da a hoto, har ya yi gwamnan Kano ya gama, babu ofishin first lady da matan gwamnoni ko shugaban ƙasa ke shiga.
Wannan dai na ganin wani sabon abu da Kwankwason ya zo da matarsa wajen taro a lokacin da ta rufe fuskar ta da niƙabi.
Kwankwaso ya daÉ—e ya na sukan tsohon gwamnan Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje, bisa yadda uwar É—akin Ganduje Hajiya Balarabe ke tsoma baki a siyasar Kano.