fidelitybank

A karo na farko ƙungiyar farar hula a Edo sun yi wa Tinubu zanga-zanga a kan fetur

Date:

Ƙungiyoyin farar hula a Edo, sun hau kan titunan Benin, babban birnin jihar, domin nuna adawa da karin farashin man fetur da aka yi a baya-bayan nan.

Kafar talabijin ta Channels ta ruwaito cewa, masu zanga-zangar sun bi ta wasu manyan tituna suna yin Allah-wadai da karin da kuma tsadar rayuwa a Najeriya.

Masu zanga-zangar dai sun ce abin na ci musu tuwo a kwarya inda suka soki matakin karin farashin man fetur yayin da ake fama da tsantsar talauci.

Masu zanga-zangar na dauke ne da kwalaye masu rubuce-rubuce daban-daban, sun kuma yi watsi da shirin tallafin Naira 8,000 da Gwamnatin Tarayya ke yi shirin yi bayan cire tallafin man fetur ɗin.

Zanga-zangar ta zo ne makonni bayan da shugaban kasa Bola Tinubu ya bayyana cewa an cire tallafin mai. Tun bayan nan kuma farashin kaya da man fetur suke hauhawa a fadin kasar.

Yayin da gwamnatin tarayya ke cewa matakin an dauka ne don ci gaban kasa, masu suka na ganin zai jefa kasar cikin mawuyacin hali.

A ci gaba da daukar wannan mataki, gwamnatin tarayya ta bayar da shawarar bayar da tallafin Naira 8,000 ga ‘yan Najeriya amma daga baya ta ce za ta sake duba lamarin bayan sukar da shirin ya sha.

Gwamnati ta yi kira ga ƴan Najeriya su yi hakuri kuma ta ce ana daukar matakan rage radadin cire tallafin.

vanguard newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp