fidelitybank

A kalla mutane 20 ne suka mutu a zanga-zanga

Date:

Wani rahoto ya bayyana cewa, mutane ashirin ne suka rasa rayukansu sakamakon tarzoma da ta ɓarke a yayin gudanar da zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a ƙasar nan.

Rahoton wanda kamfanin Beacon Consulting, mai nazari kan tsaro ya fitar ya yi nuni da cewa an kashe mutanen ne a jihohi shida da ke faɗin ƙasar.

A cewar rahoton an samu ɓarkewar tarzoma ne a jihohi 10 da suka haɗa da Adamawa da Borno da Gombe, da Jigawa da Kaduna da Kano da Kebbi da Nasarawa da Neja da kuma Yobe.

Kamfanin ya ce jihohin da aka samu rashin rayuka sun haɗa da Neja inda aka kashe mutum shida, sai jihar Borno inda aka kashe mutum huɗu, da Kaduna inda mutum uku suka rasu.

An samu rahoton mutuwar mutane huɗu a Jihar Kano, inda aka kashe mutum ɗaya a Kebbi, sannan mutane biyu ne suka mutu a Jihar Jigawa.

Rahoton ya ƙarƙare da cewa jami’an tsaro sun gaza a yunƙurinsu na tabbatar da cewa zanga-zangar ta gudana ba tare da tashin hankali ba.

“Ranar farko ta zanga-zangar ta nuna cewa jami’an tsaro da jami’an gwamnati sun yi ƙoƙarin hana zanga-zangar ko kuma tabbatar da an yi ta cikin lumana amma hakan bai yi nasara ba sakamakon yawan Jama’a da suka fito zanga-zangar a jihohi da dama.”

Har yanzu dai hukumomi ba su fitar da alƙaluma a hukumance ba kan lamarin

network news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp