fidelitybank

A iya hukunta Abdulmalik a gaban bainar jama’a – Aisha Buhari

Date:

Uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari, ta bukaci da a hukunta mai makarantar nan Abdulmalik Muhammad Tanko, wanda ya yi garkuwa da wata dalibar da ke karkashin kulawar sa Hanifa Abubakar tare da kashe shi.

Tanko, wanda shi ne mallakin makarantar Noble Kids Academy, dake Dakata a Kano ya amsa laifin yin garkuwa da ita tare da kashe karamar yarinya da gubar bera.

Uwargidan shugaban kasar ta bayyana a shafinta na Instagram da aka tabbatar, domin nuna goyon bayanta ga kiran da fitaccen malamin addinin musuluncin nan na Kano, Malam Abdalla Gadon Kaya ya yi, wanda ya bukaci a hukunta Tanko a bainar jama’a.

Aisha Buhari ta rubuta “Muna bayan mallam.” A cewar ta.

A cikin wani faifan bidiyo, Gadon Kaya ya tuhumi shugaban kasa Muhammadu Buhari da gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje da cewa “A kashe Tanko kamar yadda ya kashe Hanifa.”

Gadon Kaya ya ci gaba da cewa, ran Tanko bai fi na kananan yara ba, domin haka a kashe shi a fili.

Haka kuma masu makarantu masu zaman kansu sun yi kira da a gurfanar da abokin aikinsu wanda ya kashe ta.

An yi ta cece-ku-ce game da kisan Hanifa, inda # JusticeForHanifa ke yawo a kafafen sada zumunta a kwanakin nan.

An yi garkuwa da Hanifa Abubakar a ranar 4 ga Disamba, 2021, kuma an kashe shi bayan makonni biyu; An tsinci gawarta bayan binne ta a harabar makarantarta ta.

‘Yan sanda sun kama Tanko ne a lokacin da yake kokarin karbar kudin fansa Naira miliyan 6 da ya nema daga iyayen karamar yarinya Hanifa.

daily sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na É—aukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

ÆŠanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa Æ´an Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa Æ´anbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen Æ™auyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faÉ—a ADC

Tsohon É—an jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

ÆŠan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp