Kungiyar Gwamnonin Najeriya, NGF, ta yi kira da a gudanar da cikakken bincike kan harin da aka kai da jirage marasa matuka a Tudun Biri, karamar hukumar Igabi, jihar Kaduna.
Shugaban kungiyar, Abdulrahman Abdulrazak, ya yi magana a ranar Alhamis a Kaduna lokacin da ya jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar kan lamarin.
Gwamnan Jihar Kwara, wanda ya zo a madadin Gwamnonin Tarayya 36, ya ce za su tabbatar an gurfanar da wadanda aka samu da laifi a gaban kuliya.
Gwamna Uba Sani ya godewa shugaban NGF bisa nuna goyon baya da hadin kai a lokacin da jihar ke cikin bakin ciki.
Ya kuma mika godiyarsa ga abokin aikin sa da ya kawo ziyara Kaduna domin jajantawa gwamnati da jama’a.
NAN ta ruwaito cewa wannan mummunan lamari wanda ya faru a ranar Dec.3,2023, ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama, tare da jikkata wasu da dama.