Jamâiyyar PDP a jihar Gombe da kungiyar Atiku a zaben 2023, sun yi kira da a gudanar da bincike na gaskiya kan harin da aka kai ofishin ta.
A safiyar ranar Talata, ne aka lalata ofisoshin biyu, tare da yin awon gaba da wasu kadarori kafin a kona ofishin.
A cewar mai kula da yankin, Dr. Ali Bappayo Adamu, ya ce sun samu kiran masu gadin ofishinsu cewa, wasu sun mamaye ofishin su gaba daya, da misalin karfe 02:00 na rana. Ya ce, sun yi asara da yawa a harin tare da kwashe wasu naâurorin sanyaya daki.