Ƙungiyar kare hakkin bil’Adama ta Musulunci a ƙasar nan (MURIC), ta buƙaci a gudanar da addu’o’i a masallatai da coci-coci a ƙasar kan abubuwan da ta kira da munanan alamu a harkokin siyasar Najeriya.
Babban Daraktan ƙungiyar, Farfesa Ishaq Akintola ne ya gabatar da buƙatar a wata sanarwa da ya fitar a yau Alhamis.
Ƙungiyar ta nuna cewa yin adduo’i a masallatai da majami’u bukata ce da ta zama dole bisa la’akari da yadda baƙin al’amuran ke neman zama barazana ga makomar kasar baki ɗaya.
Saboda haka MURIC ta yi kira ga dukkan limaman Musulmi da su jagoranci mabiya a masallatansu a gobe Juma’a 9 ga watan Agusta, su yi addu’o’in, kamar yadda su ma limaman Kiristoci, su jagoranci mabiyansu wajen yin addu’ar a ranar Lahadi mai zuwa, 11 ga Agustan.
Farfesa Akintola ya ce waɗannan abubuwa na tashin hankali da suka lullube matasa a duniya, munanan alamomi ne da suke matuƙar buƙatar yi wa Najeriya addu’o’i.
Shugaban ya kuma ce su ma masu mulki akwai buƙatar yi musu addu’a ta samun kariya da kuma sanya tausayin talakawa wajen gudanar da mulkinsu.
Ƙungiyar ta MURIC, ta yi kiran ne sakamakon zanga-zangar lumana da ta rikiɗe ta zama tarzoma -ta kashe-kashe da lalata dukiyar al’umma wanda ta ce, ƙasar na cikin mawuyacin hali.
Baya ga wahalhalun da ke tattare da durƙushewar tattalin arziƙi, zanga-zangar matsin rayuwa na ci gaba da fito da wasu al’amura marasa daɗi, ga ƙasar in ji ƙungiyar ta MURIC.
Sanarwar ta kara da cewa hatta masu shirya zanga-zangar ba su yi tsammanin irin wannan mummunan lamari zai faru ba.