Tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa, Peter Obi ya ce gindaya sharuɗa kan tarukan raba tallafi zai sa ƴan Najeriya da ƙungiyoyi su rage taimakon al’umma.
Peter Obi ya bayyana haka ne bayan babban sufeto janar na ƴansandan Najeriya ya yi kira ga ƙungiyoyi da ɗaiɗaikun mutane da su riƙa sanar da ƴansanda tare da bin dokokin shirya taruka a duk lokacin da za su raba tallafi.
Shugaban na ƴansanda ya bayyana hakan ne bayan turmutsutsu wajen rabon tallafi ya jawo asarar rayuwa da dama a ƙasar, wanda Obi ya ce hakan zai sa gwiwar mutane ta yi sanyi wajen taimakon al’umma.
Tashar Channels ta ruwaito Obi yana cewa, “duk da cewa kashedin yana da muhimmanci, hakan zai a wasu su daina taimakon al’umma. Maimakon a ce dole mutane su nemi izini kafin su taimakawa mutane, zai fi kyau a ba su shawara su ɗauki matakan kauce wa turmutsutsun.”